Thursday 27 July 2017

TIR! DA MUJALLAR CHARLIE HEBDO



TUR! DA MUJALLAR CHARLIE HEBDO

DAGA

MUDASSIR ALIYU YUNUSA
NTA ZARIYA
mudassiray@gmail.com

Addini shi ne hanyar rayuwa
bisa bautar wani abun bautawa,
ta hanyar amfani da tsare-tsaren da
wannan abin bautar ko kuma
makusantansa suka tanadar
domin tafi da rayuwar yau da
kullum bisa wasu tanaje-tanaje
ko tsare-tsare. Addini ya rabu
gida daban-daban, kamar yadda
masana addini su ka yi bincike
kuma su ka tabbatar, wanda a tsarin bauta kowa nada 'yancin yin addininsa ba tare da cin zarafi ba, kuma a ka'ida bai kyautuwa ga mabiya addinai cin dunduniya ko aibata wani ko wasu ginshikai na wani addinin daban. Misali, addinin musulunci wanda ya bukaci bawa ya mika wuya kacokan ga Allah ubangijin Halittu, da kuma yin imani da manzon Allah Annabi Muhammad (Tsira da aminci su tabbata a gareshi) da kuma kafatanin annabawa da manzannin Allah. Haka kuma musulunci ya haramta zalinci akan kowa ba kadai sai iya mabiya addinin ba, baya halatta ga musulmi na kwarai ya cutar da wani ko wasu al'ummar da basa bin addinin ballantana kuma mabiya addinin bai daya, yin hakan ka iya jawo fushin ubangijin saboda irin zaman lafiya da masalahar da ke cike a cikin addinin na musulunci. Hakazalika a addinin kiristanci dana yahudanci, tanade tanaden addinan tun asali basu bada damar suka ko cusgunawa wasu mabiya addinan da suka sha bamban da nasu ba.
Zance na gaskiya addinin musulunci ya koyar da yin da'a, biyayya da kuma yarda da dukkan annabawa da mursalan da Allah (SWT) ya aiko su tun daga Annabi Adam (AS) har zuwa cikamakonsu kuma jagoransu Annabi Muhammad (SAW), wanda rashin  yin imani dasu ka iya ruguza musukuncin dan adam.
Tun a shekarun baya a yankin turai ake samun wasu tsagerun mutane da suka himmatu wajen cin zarafin musulmai ta hanyar rubutu ko zanen mutum mutumin don yin izgili gaAnnabin Allah don dai kawai a kuntatawa musulunci da musulmai wai suna Ikirarin 'yanci ne na magana ko kuma 'yancin yan jarida ya bada wannan damar. Ai wayewa ba hauka bace, kuma wannan lamarin duniya ta san cewar ana aiwatar dashi ne don a turawa mabiya addinin musulunci haushi duk da suna batun 'yanci to ai harda 'yancin gudanar da addini ga jama'a a fadin duniya. Duk da sanin rashin dacewar abin amma jagoranci duniya bai daukar wani kwakkwaran mataki ganin yadda abin ke ta da hankulan mabiya addinin na musulunci. To wai me ake nufi da musulmin duniya? Na farko dai ina dalilin yin wannan batancin? Shin takalar fada akeyi ko kuwa so ake a nunawa duniya musulunci ba a bakin komai yake ba?
Kamar yadda na fada a farko babu addinin da ya aminta aci zarafin wasu masu bautar daban,  to in haka ne me zai sa shuwagabannin irin wadannan sakarkarun mutanen baza su ja musu kunne ba su kuma nuna rashin a mincewarsu karara. Ni kam nayi imanin musulmin kwarai ba zai taba munzata wani ko wasu don kawai suna da banbancin addini, kai koda kuwa hakan ta faru to zakaji malaman muslunci sun fito sun soki abin. Kodayake Kalilan daga mabiya addinin kiristanci sun yi tur da ayyukan batancin, sai dai tun a shekarun baya da hakan ta faru a kasar Denmark har ila yau abun kara bayyana yake kuma wannan shine dalilin da ya tunzura wasu matasa daukar hukuncin da hannunsu. Duk da yake daukar hukunci ko doka ahannu ya saba da ka'idar musulunci amma bai kamata a bar dukan jaki a koma taiki ba, inda tun farko an dauki matakin hanasu yin irin wannan tabargazar to da hakan bata faru ba. Don kuwa a gaskiyar lamari babu addinin da zai saka ido ana masa cin kashi haka, kuma nayi imanin banda musulmai suna da hakuri da tuni fitinar ta girmama.
Da haka nake Tur da wannan cin zarafin Manzon Allah(SAW) da mujallar Charlie Hebdo dama sauran kafafen da ke aikata irin wannan badaqalar. Ina kuma jawo hankulan 'yan uwa musulmai dasu cigaba da addu'ar Allah wadai su kumayi tir da nuna damuwarsu karara. Sannan kuma shugabannin musulmai su hada kawunansu su rika magana da murya daya tak don kawar da ire iren wadannan cin zarafin da izgilanci da gangan  dole ne musulmai su kyamaci wannan badakalar su kuma sanya babbar alamar dakatarwa da zata hana cin zarafin al'ummarsu, addininsu da kuma uwa uba Annabinsu (Tsira da Amincin Allah su tabbata a gareshi). Allah ka qarawa Annabi daraja, wasila da fadila ameen.

Mudassir ya rubuto daga NTA Zariya

No comments:

Post a Comment