Thursday 27 July 2017

A DUBA TITUNAN KASAR NAN



A DUBA TITUNA DA HANYOYIN KASAR NAN
DAGA:
MUDASSIR ALIYU YUNUSA
mudassiray@gmail.com

Sufuri wani abune mai matukar mihimmanci a rayuwar al'umma, cigaban kowacce kasa baya samuwa sai an sami ingantattun hanyoyin sufuri kama daga hanyoyin mota, layin dogo, sufurin jiragen sama dana ruwa da kuma sauran hanyoyin da ke taimakawa al'umma wajen zirga zirga a cikin kasa.
A Najeriya mafiya yawan jama'a sun fi amfani da Sufurin motoci wajen gudanar da tafiye tafiyensu na safarar kasuwanci, neman ilimi, zimunci da sauran ayyuka da sabgogin rayuwa. Sai dai a halin yanzu lalacewar manya da kananan hanyoyin mota a fadin kaaarnan ta zamo babbar annoba da kalubale musamman yadda yawa yawan titunan kasar sun tsufa wasu sun mutu murus wanda hakan ke da alhakin kawo munanan hadura dake jawo asarar rayuka, lafiya da dukiyoyin jama'a maras adadi. Wannan al'amarin ya kasance abun damuwa kuma abun takaici musamman ganin yadda Allah ya huwacewa kasar nan mamakon arziki wanda ya kamata  ace tun  tsawon shekaru 56 maganar samar da ingantattuun hanyoyin sufuri musamman tituna an gama dasu, sai dai kash! Barna, wawaso da kuma tsananin son zuciya na jagororin kasar yasa ake  fuskantar halin kunci da  tabarbarrewar al'amura a halin yanzu.
A dukkan bangarorin kasar nan yawa yawan hanyoyin da suka hada manyan garuwa da jihohi suna matukar bukatar gyara ko sabuntawa. Misali a arewacin Najeriya hanyoyin da suka hada da Gombe zuwa Yola, Kaduna/saminaka zuwa Jos, Kano-Zariya-Kaduna har zuwa Abuja, Zariya -Funtuwa - Gusau zuwa Sokoto da sauransu suna bukatar agajin gaggawa daga gwamnatin tarayya da ma na jihohi don ingantasu. A shekarun baya hukumar dake da alhakin kula da gyaran tituna(FERMA) tana iya kokari wajen yin kwaskwarima da  garanbawul a manya da kananan tituna a fadin kasarnan, sai dai yanzu kam ba  amo ba labarin ta lamarin da wasu Kewa kallon gazawar gwamnati wajen gina sabbin hanyoyi, gyaran tituna da gadoji.
Shawara ta anan itace tunda yanzu Kasar na fama da matsalar tabarbarewar tattalin arziki wanda ake ganin  ya jawo rashin gabatar da wasu ayyukan cigaba, me zai hana gwamnati ta dawo da tsarin karbar harajin hanya da ake bayarwa ada (Toll Gate) don a rika amfani da kudaden don gyaran hanyoyin. Gwamnati da hadin gwiwar kungiyoyin masu amfani da tituna su sanya ido wajen tattara kudaden da aka karba a hannun masu ababen hawa musamman a manyan hanyoyi don tabbatar da ana gyara da kula da titunan akai akai. Wannan zai sai dole a rika gyaran hanyoyin lokaci zuwa lokaci wanda rashin yin hakan ka iya jawo tuhuma daga masu ababen hawa dake amfani da hanyar, hakan kuma ka dakile daukar lokacin da ake ba tare da kula da titunan ba.
A karshe ina kira ga gwamnatocinmu dasuyi gaggawar kaiwa manyan titunan kasar nan agajin gaggawa don rage yawan afkuwar hadura a dalilin rubewar tituna.
MUDASSIR ya rubuto daga NTA Zariya.


No comments:

Post a Comment