Thursday 27 July 2017

MARIGAYI NAJIB ALIYU YUNUSA





MARIGAYI NAJIB ALIYU YUNUSA
 (1982 - 2012);
DAN UWA RABIN JIKI.

DAGA:
MUDASSIR ALIYU YUNUSA
NTA ZARIYA
        mudassiray@gmail.com

Tabbas dukkan mai rai mamaci ne kamar yadda Allah madaukakin sarki ya bayyana mana a cikin littafinsa mai tsarki, haka kuma hausawa na cewa "duk wanda ya sanya taguwar rayuwa to dole mutuwa zata tube ta ko ba dade ko ba jima". Wannan ya tunamin da amshin wakar rayuwa ta Fati Rayuwa inda take cewa " Rayuwa tana faruwa wucewa take kamar ba ayiba". Wannan shine yadda Allah ya tsara, shi yasa a cikin suratul mulk ya ambaci halittar mutuwa a farko kana ya ambaci halittar rayuwa daga bisani.
Mutuwa nada ciwo, takan sanya shiga rudani da dimuwa tsawon lokaci musamman ga makusantan mamacin. Tabbas na gaskata hakan shekaru 5 da suka shude sakamakon rashin dan uwana na jini na jika wanda akasarin rayuwata tare mukayi tun muna yara tun bamusan ciwon kanmu ba balle na jiki. Marigayi Najib shine tsara na da na bude ido na gani a tare dani, komai na yarinta tare muke gabarta dashi kama daga cin abinci, wanka, wanki, wasa, bacci da zuwa makarantar allo da islamiyyar dare da yamma. Rana daya aka sanya mu a makarantar firamare, lokaci daya aka kaimu  cikin makaranta daya, idan an fito tara(9) tare muke cin abinci sannan muyi tsalle tsalle a lokacin takaitaccen hutun daukar darasi (short break), sannan in an tashi mu hallara a waje daya don jiran me kaimu gida. Haka abun ya cigaba da gudana idan muka dawo gida, daki daya muke kwana tsawon shekaru 25 har zuwa lokacin da na tafi bautar kasa a Jihar Borno, shi kuma jim kadan ya sami sauyin wajen aiki daga Kano zuwa Abuja.
An haifi Marigayi Najib Aliyu a unguwar Tarauni dake karamar hukumar birnin kano( yanzu karamar hukumar Tarauni) a ranar 19 ga watan mayu, 1982. Ya fara karatun muhammadiyya a makarantar allo ta mallam Bature dake Tarauni da kuma makarantar islamiyya ta da'awa dake Sulaimanu Crescent duk a cikin Kano. Ya shiga makarantar firamare ta Magwan Model Primary School a 1990, bayan kammalawa ya shiga karamar sakandire dake Sabuwar Kofa Kano, daga nan ya wuce kwalejin Rumfa dake Kano inda ya samu shaidar kammala sakandire ta SSCE a shekarar 2001. Ya samu gurbi a kwalejin ilimi ta gwaunatin tarayya dake Kano (FCE Kano) a wannan shekarar inda ya sami shaidar NCE a sha'anin kasuwanci (Bussiness Admin) a 2005. Ya fara aiki a 2007 da gidan man Sani Brothers Petroleum na rukunin kampanin Sani Brothers Transport Ltd, a matsayin mai kula da kudi (Cashier), ya samu cigaba inda ya zama shugaban gidan man na dai kampanin a babban birnin tarayya Abuja, mukamin da ya rike tsawon shekaru 4 har zuwa lokacin rasuwarsa. Ya kuma ci gaba da karatunsa na digiri a jamiar Abuja dake  Gwagwalada. Marigayin ya taimakawa jama'a da dama wajen yi musu hanyar samun aiki a gidajen man kamfanin dama sauran wurare.
Marigayi Najib mutum ne na jama'a me girmama na gaba dashi, mai mutunta abokansa, mai barkwanci ga yara, mai tsananin sada zumunta ga yan uwa na birni da na kauye sannan kuma uwa uba matashi ne mai riko da addini. Shakuwarmu dashi takai makura don duk da ina aikina amma bai kula da hakan ba don a duk lokacin azumi sai ya bani kyalle na tufa don yin dinkin sallah. Haka zalika a lokuta da dama in zai zo ganin gida daga Abuja, nakan jira shi a Kaduna ko Zaria har sai yazo ya dauke ni zuwa Kano, lamarin dake bamu damar tattauna batutuwan da suka shafe mu da 'yan uwanmu da ma hirar rayuwa.
Labarin rasuwarsa ta tayar da hankulan 'yan uwa, abokan karatunsa da na aikinsa, makotansa, malamansa da sauran jamaar gari.
Ya rasu ranar juma'a 18 ga watan Mayu, 2012 a dai dai lokacin da jama'a ke amfana da dimbin kyautatawarsa a garesu. Ya amsa kiran ubangijinsa ya bar mata daya da yaro daya (Ahmad Najib), iyayensa da yan uwansa maza da mata 19. Allah ya gafarta masa ya kyautata namu zuwan ya kuma albarkaci abinda ya bari. Yan uwa da abokai kuma Allah ya kara mana  hakuri da juriyar wannan rashin. Amin.
MUDASSIR ya rubuto daga NTA Zariya.

No comments:

Post a Comment